Skip to main content

Posts

Showing posts from June, 2017

Babi na sha bakwai : Sadaukarwar Núsi

Nan take abubuwa da dama, musamman hikayoyi da suka shafi wannan mutun-mutumi dake wannan waje, suka fara kai-komo acikin ranta. Cikin tsammani ta buɗe baki da niyyar fara yi masa tambayoyi, to amma da yake shima kamar sunyi anko ne, domin babu abinda ke kai-komo a zuciyar ta, banda tambayoyin nan guda biyu; wai shin wanene wannan yaro da har ya isa ya ga mutun mutumin Daikirin, kuma daga ina ya fito? Hakan ne yasa duk su biyun sukai anko wajan buɗe bakunan su da niyyar yiwa juna tambaya, amma a dai-dai wannan lokaci ne kwatsam babu tsammani idanun Armad suka rufe ruf, sannan babu alamar rai a tattare dashi, ya faɗi kasa da ƙarfi a sume. Kallo ɗaya kacal zakai masa kasan yayi zazzafan suma ne irin wanda bashi da nisa sosai da mutuwa. Cikin tsananin mamakin abinda ke faruwa da Armad tayi firgit ta matsa daga kusa dashi zuwa nesa, inda ta zauna tana haki. Ta dubeshi cikin mamaki da firgici zuciyarta cike da tunanin maike faruwa ne, kuma mai ya kamata tayi? T...

Babi na sha shida : Ido da Ido da Daikirin

''Shekara uku!!'' Armad yai ajiyar zuciya gami da ƙurawa wannan budurwa ido cikin mamaki. ''Ba zan iya yin shekara uku anan ba, saboda akwai abinda nake so nayi sauri nayi, na koma gida. Dan ALLAH yi min cikakke bayani naji abinda ke faruwa da wannan waje.'' Kallonsa kawai tayi na ɗan lokaci, kafin daga bisani ta girgiza sannan ta ja dogon numfashi gami da ɗaga yatsanta na dama inda ta nuna masa filin dake gabas dasu tace, ''hanyar fita daga wannan waje tana can ɓangaren. ''Daga nan kuma zuwa wajen baifi tafiyar awa ɗaya ba. ''To amma kayi sani cewa gaba ɗaya wurin nan a zagaye yake da wani sinadari mai suna Negrinki. ''Wanda shi ne babban dalilin daya sa baka ga kowacce irin halitta anan duniyar ba. ''Kasancewar shi wannan Negrinki yana iya zuƙe ran duk wani abu mai rai. ''Kuma babban tashin hankalin shi ne iyakacin yadda ka kusance shi, iyakacin yadda zaka fuskanci ƙarfinsa. ''Mafi ƙanƙant...

Babi na sha biyar : Sanyin Babban Sihiri

A can wannan daji kuwa duwatsu ne iyakacin hangen ɗan-adam, inda daga cikinsu mutane sanye da kayan yaƙi suke ta ƙara ɓulɓulowa su na nufo wajan da su Zahra suke tsaye cirko-cirko tun bayan jin wannan murya. Kafin kace meye wannan mutane da dama sun kewaye su ta kowanne ɓari. Ana cikin haka wasu manya-manyan mutane waɗanda su kaɗai ne fuskarsu bata naɗɗaɗe da rawani suka fito fili daga bayan wasu jajayen duwatsu. Su na fitowa, kai tsaye suka fara kusantar inda su Hasanu suke tsaye. Dukkaninsu manya-manyan halittu ne tayadda in baka kula ba sosai ba, sai kace samudawa ne. Na tsakiyar tasu ya ɗan ɗara ragowar tsayi yana sanye kuma da jan rawani wanda kamar kamar rawanin sauran mutanen dake kewaye da wajan ba, bai rufe masa fuska ba. Yana ɗauke da wani ƙatoton farin gatari. Idan kuma ka duba zakaga cewa duk da duhun wajen bai hana idanunsa walƙiya ba, wanda idan ka ƙura ido zaka fahimci cewa acikin idon nasa akwai waɗansu abubuwa guda biyu acikin kowanne ido. Idan ka ƙara ...

Babi na sha hudu : Ikenga O Bayajidda

AA shekarar 1851 After Amri (A.A), a wani gari mai suna Jíha, dake kan doron ƙasa ta bakwai ɓangaren Arewa. Tsakiyar dare ne, kuma a wannan rana ma wuni akai ana azababben yaƙi tsakani ɓangaren Ururu da kuma ɓangaren ƴan adawa dake da shalkwatarsu a wannan gari. Babu abinda kake gani sai gawarwakin jama'a duk inda ka duba, dan kusan a wannan rana zaka iya cewa aka kawo ƙarshen wannan babban yaƙi. Wannan yaƙi dai shi ne wanda mahaifiyar Armad ta samu rauni ashi, kuma harma Armad yaci alwashin sai ya kawo mata mutumin data fita nema ta samu wannan ciwo har gida, komai rintsi komai wuya. To acikin wannan gari dai, duk inda ka kalla gawarwaki ne a kwance fululu, amma duk da haka idan ka samu ɓangaren da ba mutun a kwance, zaka ga cewa gaba ɗaya ƙasar wajen ta juye izuwa launin ja da baƙi, saboda yawan jinin daya kwarara a wannan rana. A ƙasa kaɗai al'ummar dake kwance a mace sun haura dubu ɗari, wani ba kai, wani ba ƙafa, wani kayan ciki a waje, wani a caccake da takubba,...

Babi na sha Uku : Wacce Shekara Muke wannan??

Tun bayan ɓacewar Armad daga wannan waje, hankalinsa ya dusashe ta yadda shi kansa bayan farkawarsa bai san a inda yake ba, bai san kuma tayadda yaje wajen daya farka ya tsinci kansa ba, sannan kuma bai san kwana nawa yai ba, tun bayan dusashewar hankalinsa ba. Amm abu ɗaya da yake iya tunawa shi ne, gab da kafin hankalinsa ya dusashe, ya kasance yana ta kai-komo da abubuwan sirrin da yaji daga wannan murya wadda take magana akan Rukunai guda biyu na Ururu. Sirrin da Armad ya tabbatar indai ya fita to lallai sai ya rikita dukkan duniyar ƙasa bakwai, tayadda zaman lafiya ma zai iya zuwa ƙarshe!! Da farkawarsa abinda ya fara yin arba dashi shi ne fili fetal gabas da yamma, gudu da arewa ko ina ya duba baya iya gano ƙarshensa. Babban abun mamaki da wannan waje shi ne babu alamun wata halitta a wajen ko kaɗan; kama daga kan namun daji zuwa tsirrai zuwa tsuntsaye, ko'ina ka duba ba komai a wajen kawai sai fili fetal da tsandaurin ƙasa. Sai dai kuma Armad bai shiga al'ajabin ...

Babi na sha biyu : Urúrú

Kwanaki huɗu bayan ɓacewar Armad bayanda yayi amfani da wannan hatasabibiyar hanya ya ceto su Zahra daga wannan baƙin ruwa da shuɗin Dordor ya harba musu. Zahra tayi shiru su na tafiya bata kuma yiwa kowa magana ba tun bayan tahowar tasu, duk da kuwa ƙoƙarin kwantar mata da hankali da Hasanu yayi tayi, kai hatta Kiru ma da ya nuna aniyarsa a fili ta so ya halaka Armad a baya, sai da ya sauko ya kuma fara lallamar Zahran yana gaya mata cewa shi dai bai gane mene ne a tsakaninsu ba, amma koma mene ne ta gane cewa, Armad ba irin mutanen da zasu mutu cikin sauƙi ba ne, ya kuma gaya mata da Armad ɗin zai iya mutu da wuri aida tuni ya rigaya ya halaka shi da farar takobinsa. Ya gaya mata hakan ne da wasa duk da niyyar ko zata ɗan saki fuska, amma ina ko kaɗan bata ma nuna ta jishi ba, idanunta kawai na nuna nutsawa acikin tsananin tunanin wani abu ne kawai. Tun da farko bata yarda sun baro wajan ba sai da suka kwashe awa ashirin da huɗu cir, tana kallon wajan da Armad ya ɓace. Babu yad...

Babi na Sha ɗaya : Dordor

Dordor!! Wannan suna ne wanda jama'ar wannan zamani suka laƙabawa waɗansu halittu, waɗanda ba mutane bane, hasalima a zahiri fatalwowi ne. Sai dai kuma amma su na da irin sura ta mutane sak, in banda waɗansu banbance-banbance da suka raba. Girmansu ya haura na mafi yawancin mutane misali, tsaka-tsakinsu sune waɗanda girmansu yakai kimanin girman ƙarti biyu na mutane a haɗe. Kalar fatar jikinsu zata iya ɗaukar kowacce irin kala, kama daga kan baƙi, fari, ja, kore, shuɗi kai dama dukkan sauran launuka. To ɗaya dai daga cikin irin waɗannan fatalwowi ne, ya nufo Armad ta baya, da tsananin muguwar niyya taya halaka shi. Kuma shi ne wanda Hasanu ya gano yana tahowa tunda farko, kuma shi ne dai wanda Zahra/Nostalgiya ta gani, lamarinda yasa take ta ƙoƙarin janyo Armad waje. A dai-dai lokacin da Armad ya waiwaya, sukai ido biyu da wannan fatalwa, mai suna Dordor, kamanninta suka shiga kwakwalwarsa. Nan take yasan cewa lallai a kowanne lokaci, mutuwa zata iyai masa sallama idan baiy...

Chapter ten : Gimbiya Zahra

Daga gefe, idanun Hasanu da wannan budurwa acike suke da mamaki, kuma zuwa wannan lokaci su na da cikakkiyar masaniyar cewa shima Armad, koma daga ina yake, lallai ya sami horo na musamman. Dukkaninsu sun san irin ƙarfin da farar takobin Kiru ke dashi, amma bisa mamakinsu Armad ya iya tare sara daga gareta kuma ba tare da yaje ƙasa ba. Hasanu ya ja numfashi sannan ya ƙara matsawa gaba, gami da ƙara ƙurawa Armad ido. Ya kalleshi sama da ƙas, sannan bayan wani ɗan lokaci sai kawai idanunsa suka canja, kamar wanda yake so yaga wani abu a tattare da Armad, amma kuma ya kasa. Yana shirin ɗauke ido daga kan Armad, sai idonsa yakai kan wannan jan ƙyalle dake ɗaure a gaban goshin Armad. Nan take ya ƙura masa ido tsahon daƙiƙu, kafin kwatsam idonsa ya cika da firgici sannan jikinsa ya fara karkarwa. Cikin ɗimuwa ya fara magana aciki, "madauwamiyar Miyura... ina ba abu bane mai yiwuwa... to amma... ''Hmmm.... ko madai ba ita bace a goshinsa ba, kashe shi a yanzu gangan...