Skip to main content

Posts

440-445

 Shísu yayi shiru yana tunani. Bai taɓa gwada fasaharsa a irin wannan yanayi ba, amma kuma abu ne mai yiwuwa. Tunda yana iya amfani da tunaninsa ya motsa ƙarfe ai kuwa zai iya ƙara masa gudu ko kuma ya rage. Kamar yadda yake ture masu da kibbau idan an harbo masa. Sai dai kuma yana jin tsoro kada yace zai iya kuma sai lokaci yazo ya kasa. Hakan zai iya sanadiyar mutuwar Asifu dama sauran wanda suke tare dasu. Shin mai zai cewa Nusi-ya idan hakan ta faru?  "Ban taɓa... yin hakan ba, amma ina ganin watakila..."  Nusi ta ɗora hannu a kafaɗarsa lamarinda yasa ya daina kinkina.  "Zaka iya," inji Nusi. "Ni nasan zaka iya." Shísu ya risuna cikin girmamawa. Tabbas tunda Nusi-ya tace zai iya to kuwa zai iya. Bazai bata kunya ba komai rintsi komai wuya. "Zan iya," inji Shísu. "Amma yaya zaku yi da ƙusar mairakana?" Inji Armad. A ganinsa babban abinda yake ƙarawa denizawa ƙarfi shi ne fasahar mairakana. Koda Asifu zai iya yanka jikin Iluru bazai s...

434-439

 Ayubu ya fuskanci mutun-mutumi irinsa guda huɗu. Dukkansu kamar su ɗaya da Armad sak. Kai zaka iya cewa dukkansu Armad ne kawai da zuciya daban-daban. "Butulu," inji Armad 1. "Shugaban mu shi ne ya halicce ka sannan kuma ya raya ka, amma ka butulce masa. Kai kuwa yaya kake ji a ranka?" Armad 2 da Armad 3 da Armad 4 suka haɗa baki suka amsa da cewa, "butulu, butulu, butulu."  Maimakon yaji haushi sai Ayubu ya fashe da dariya.  "Nasan abinda kuke ji a ranku," inji Ayubu. "Kuna jin imani da soyayyar Armad. Kuna so ku faranta masa, bakwa son yin duk abinda zai ɓata masa rai. Umarninsa kamar ibada ne a wajen ku. Haha.. akwai lokacin da nake jin dai-dai irin abinda kuke ji a yanzu. A hankali idan kuka rayu zaku gane gaskiya. Hankalinku zai dawo ku fuskanci tunanin ku na yanzu ba dai-dai yake ba. Abu na farko da zaku gane shi ne Armad mutun ne kamar ku. Dan me shi zai rayu ku kuma ku mutu? Na tabbata kuna son rayuwa, ko ba haka ba?" Armad 3 d...

428-433

 Abu kamar wasa sai Han'ibal ya ƙara azama wajen jifansu.  "Kuyi gaba kada ku tsaya," inji Armad. "Zan tare shi." Armad ya fita daga tawagar yayi sama ya tari Han'ibal.  "Hannun Aradu." Hannun hagun Armad ya juye izuwa walkiya ya tunkari Han'ibal. Han'ibal ya samarda tasa ƙawanyar ya tunkari Armad da ita. Suna haɗuwa aka dare aka basu guri. Tartsatsin garwashi da zafin wuta da walkiya ya feshe wajen. Ƙananun mayaƙa dake ƙasa suka fara gudu.  "Ku gudu, sarkin jinzidal ya fusata," inji wani sadauki.  Armad ya danna da karfi amma Han'ibal ya tare shi. Idan walkiyar Armad ta fara yin ƙarfi tana ture wutar Han'ibal sai kaga wutar ta fara ruruwa tana zafi. A hankali sai kaga ta danno ta rufe wutar.  Armad ya juyar ɗayan hannunsa izuwa walkiya ya kawowa Han'ibal duka. Han'ibal ya tare da wata ƙawanyar. Tururi da zafin wuta ya cika filin yaƙin. Maƙogoron mayaƙan dake kusa ya bushe. Dole aka fara neman ruwan sha amma babu. ...